Zanga-zangar adawa da juyin mulki ta barke a Guinea-Bissau
Daruruwan ‘yan Guinea-Bissau sun yi tattaki a cikin birnin Bissau, babban birnin ƙasar, domin yin zanga-zanga kan juyin mulkin soja da aka yi a watan da ya gabata tare da neman a saki shugabannin ‘yan adawa.
Masu zanga-zangar sun yi arangama da jami’an tsaro a ranar Juma’a yayin da suke kiran a saki Domingos Pereira, shugaban Jam’iyyar African Party for the Independence of Guinea and Cape Verde (PAIGC), wanda rahotanni suka ce an tsare shi ne a lokacin juyin mulkin.
Jami’an soji sun sanar da juyin mulki a ƙasar da ke Yammacin Afirka mai amfani da harshen Fotigal, kwanaki kaɗan bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa, kuma ‘yan sa’o’i kaɗan kafin a ayyana sakamakon zaɓen.
Shugaba Umaro Embaló da babban abokin hamayyarsa, Fernando Dias da Costa, duk sun ayyana kansu a matsayin waɗanda suka yi nasara tun kafin hukumar zaɓe ta sanar da sakamakon.
Daga bisani, ‘yan juyin mulkin sun naɗa Manjo Janar Horta Inta-a a matsayin shugaban riƙo.
Bayan juyin mulkin, Ƙungiyar Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta dakatar da Guinea-Bissau daga ƙungiyar har sai an dawo da tsarin mulki a ƙasar.
Ƙungiyar ta bayyana wannan mataki ne a cikin wata sanarwa bayan kiran wani taron gaggawa na shugabannin ƙasashe da gwamnatoci ta kafar intanet kan halin da ake ciki.
Ana sa ran shugabannin yankin za su gana a ranar Lahadi domin tattauna rikicin da kuma ɗaukar matakan takunkumi masu yuwuwa kan ƙasar ta Yammacin Afirka.
managarciya